2 Saboda haka Yaƙub ya ce wa gidansa da kuma dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku zubar da baƙin allolin da kuke da su, ku tsarkake kanku, ku kuma canja tufafinku. 3 Sa’an nan ku zo, mu haura zuwa Betel, inda zan gina bagade wa Allah wanda ya amsa mini a ranar wahalata, wanda kuma ya kasance tare da ni a dukan inda na tafi.” 4 Saboda haka suka ba Yaƙub dukan baƙin allolin da suke da su, da zoban da suke kunnuwansu, sai Yaƙub ya binne su a ƙarƙashin itacen oak a Shekem. 5 Sa’an nan suka kama hanya, tsoron Allah kuwa ya kama dukan garuruwan da suke kewayensu har babu wanda ya iya bin su.
6 Yaƙub da dukan mutanen da suke tare da shi suka zo Luz (wato, Betel) a ƙasar Kan’ana. 7 A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel,[a] gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa.
8 To, Debora, ungozomar Rebeka ta rasu aka kuma binne ta a ƙarƙashin itacen oak, ƙasa da Betel. Saboda haka aka kira wurin Allon Bakut.[b]
9 Bayan Yaƙub ya komo daga Faddan Aram,[c] sai Allah ya bayyana gare shi, ya kuma albarkace shi. 10 Allah ya ce masa, “Sunanka Yaƙub[d] ne, amma ba za a ƙara kira ka Yaƙub ba; sunanka zai zama Isra’ila.”[e] Saboda haka ya ba shi suna Isra’ila.
11 Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki[f], ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka. 12 Ƙasar da na ba wa Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba ka, zan kuma ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka.” 13 Sa’an nan Allah ya tashi sama daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
14 Yaƙub kuwa ya kafa al’amudin dutse a inda Allah ya yi magana da shi, ya zuba hadaya ta sha a kansa; ya kuma zuba mai a kansa. 15 Yaƙub ya kira inda Allah ya yi magana da shi, Betel.[g]
19 Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem). 20 Yaƙub ya kafa al’amudi bisa kabarinta, al’amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau.
21 Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder. 22 Yayinda Isra’ila yana zama a wancan yanki, Ruben ya shiga ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra’ila kuwa ya ji labari.
- a El Betel yana nufin Allah na Betel.
- b Allon yana nufin itacen oak na kuka.
- c Wato, arewa maso yammancin Mesofotamiya, haka ma a aya 26
- d Yaƙub yana nufin ya kama ɗiɗɗige, a habaici dai, ya ruɗi.
- e Isra’ila yana nufin kokawa da Allah.
- f Da Ibraniyanci El-Shaddai
- g Betel yana nufin gidan Allah.
- h Ben-Oni yana nufin ɗa na wahalata.
- i Benyamin yana nufin ɗa na hannun damana.